26/05/2026
TALAKAWA FA BA MUTUMEN KIRKI SUKE SO YA MULKE SU BA A NIGERIA: Case ɗin Gombe yaishi kowa aya
Duk dai ƙiyayyar ka da Pantami, ƙarya kake kace masa jahili, ko bai san me ya keyi ba, kuma duk rashin mutun cin ka, da rashin son gaskiyar ka, ƙarya kake kace wai 'yan siyasar Nigeria sun fishi ƙima da mutunci.
Kome son ranka indai shugaba a ke nema, wanda zai mulki al'umma, wanda a ke kyautatawa zato ga abun da ya bayyana ga mutane, ya cancanci ya zama shugaba, fiye da shuwagabannin da suke mulkin mu a yanzu, kai harda waɗanda s**a mulkemu a baya, kai kasan Pantami ya cancanta.
Ilimi dai yana dashi, babu wanda yake gardama ko tababa a kan wannan, ya nada ilimin addinin sa (na musulunci) garau, wannan ko shakka babu, don bar waɗanda ba suje islamiyya ba sun yarda ya nada ilimin addini.
Sannan ya nada ilimin boko, wanda da yawa wasu wawaye ma ke ɗaukar wanda bai da ilimin boko a matsayin jahili ko wawa, to Pantami yana dashi.
Mutun dai ko Professor na wasa kaji 'yan ajin su a makaranta suna kiran sa, I'm telling you ya karantu, kuma ya cancanci su nan ne, bare Professor ɗin da jami'a a Nigeria tace Professor ne.
Koba Professor bane, yau dai duk wanda dai yayi Phd. ya wuce jahili, in kana ganin abun ƙarya ne, kaje kace za kayi Phd. ka gani da idanun ka.
So, ace in banda dai Nigeria na Nigeria, wai mutum irin Professor Isah Ali Pantami, wai har wani yafito yace maka wai bai cancanci ya zama shugaba ba.
A irin jahilan shuwagabannin da suke mulkin Nigeria, masu Secondary Certificates, waɗanda Fatiha basu iya ba, da waɗanda ba'a masan ina su kayi karatu ba, karatun bokon ma fa, bana addini ba, wai a irin wannan ƙasar wani ke faɗar wai irin Pantami bai cancanci shugabanci ba.
Na taɓaganin wani yana cewa, "wai ai idan ana maganar mulki, ba maganar ilimi a keyi ba", kuma wai intellectual mutun ne, fisabilillahi, to idan ana maganar mulki maganar me a ke ? Jahilci ? Ko Jagaliyanci ?
Gaskiya guda ce, na sha faɗa, duk lalacewar Pantami, na rantse da Allah yafi waɗannan shuwa