A+A movement katsina chapter

A+A movement katsina chapter *Atiku / Amaechi Movement 2027 - Katsina Chapter*
Mobilizing Katsina people for *Jobs, Food Security, and Good Governance* in 2027. Equity. One Nigeria.

We stand for:
Competence. Join the movement.

With Cybersecurity by CyberKid – I just got recognized as one of their rising fans! 🎉
21/08/2026

With Cybersecurity by CyberKid – I just got recognized as one of their rising fans! 🎉

“Dan takarar mu na gwamna, Senator Ahmad Babba Kaita zai yi wahala ka samu wani dan jahar Katsina da yaje majalissar tar...
20/08/2026

“Dan takarar mu na gwamna, Senator Ahmad Babba Kaita zai yi wahala ka samu wani dan jahar Katsina da yaje majalissar tarayya yayi aiyukan alheri, ya kawo aiyukan ci gaban kasa, ya tsare dukiyar al’umma, ya taimaka ma mutane kamar shi a jahar Katsina”

- Senator Sirajo Aminu Makera GM

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Nigeria kuma Dan Takaran Kujerar Shugaban Kasa a jam'iyar ADC Atiku Abubakar ya sha alw...
20/08/2026

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Nigeria kuma Dan Takaran Kujerar Shugaban Kasa a jam'iyar ADC Atiku Abubakar ya sha alwashin dawo da tallafin man fetir idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaɓen shekarar 2027.

Atiku ya danganta tsadar Kayaki da Hauhawan farashi da al'ummar Nigeria ke fama dashi da cire tallafin man fetir da gwamnati mai ci tayi

TSARKI YA TABBATA GA ALLAH! 🤲A tattaunawar kai tsaye da 'yan jaridu sukayi daren jiya da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa...
20/08/2026

TSARKI YA TABBATA GA ALLAH! 🤲

A tattaunawar kai tsaye da 'yan jaridu sukayi daren jiya da tsohon Mataimakin Shugaban Kasarmu Nigeria Alhaji Atiku Abubakar, Atiku ya bayyana cewa idan ya lashe zaben shugaban Kasa na 2027, zai dawo da tallafin man fetur nan take

Idan ba mu manta ba, a ranar da aka rantsar da Maigirma Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2023 ya sanar da janye tallafin man fetur, Gwamnatin Buhari ta bar farashin man fetur a Naira ₦185, zuwa yau farashinsa ya kai Naira ₦1,300 a Gwamnatin Tinubu

A bayyane yake cewa farashin man fetur yana da matukar tasiri a rayuwar talakawan Nigeria, idan farashin fetur ya tashi, farashin sufuri, abinci, kayan masarufi da sauran bukatun yau da kullum su ma kan tashi

Saboda haka, batun dawo da tallafin man fetur ba wai batun siyasa ba ne kawai; batu ne da ya shafi rayuwar miliyoyin talakawan Nigeria kai tsaye, kusan babu wani abinda talakan Nigeria ke mora kai tsaye daga Gwamnati imba tallafin man fetur ba

Idan aka dawo da tallafin man fetur din zai rage wa talaka bala'in tsadar rayuwa da muke fama da shi a Kasarmu, zai saukaka wa jama'a wahalhalun tattalin arziki da zirga-zirga

Sannan Atiku yayi rantsuwa da Allah yace zai kwato duk kudaden da aka samu a dalilin janye tallafin mai, sannan ya hukunta duk wanda yake da hannu a karkatar da kudaden

Ya Allah Ka tausaya mana, Ka saukaka wa talakawan Nigeria halin kunci da suke ciki, Ka kawo mana shugabanci da zai zama alheri ga Kasa da al'ummarta ba don halayenmu ba, sai don RahamarKa Yaa Allah 🤲🙏

19/08/2026

National chirman of the Atiku Amaechi movement.

Leadership and ProgressThe future of any nation depends greatly on the quality of its leadership and the participation o...
19/08/2026

Leadership and Progress

The future of any nation depends greatly on the quality of its leadership and the participation of its people.

Let us continue to engage responsibly, encourage positive ideas, and support efforts that can contribute to the growth and development of Nigeria.

Together, we move forward

19/08/2026
Da ɗumi-ɗumi: Zaɓen Osun: Jonathan Ya Bukaci A Kafa Sabbin Iyakokin doka da zata hana Gwamnoni da Ministoci zuwa duk wat...
18/08/2026

Da ɗumi-ɗumi: Zaɓen Osun: Jonathan Ya Bukaci A Kafa Sabbin Iyakokin doka da zata hana Gwamnoni da Ministoci zuwa duk wata jiha a lokacin da take Gudanar zaɓe

Tsohon Shugaban Ƙasa, Dr. Goodluck Ebele Jonathan, ya yi kira da a kafa sabbin ƙa’idoji kan yadda manyan ’yan siyasa da masu riƙe da mukaman gwamnati ke gudanar da harkokin siyasa a lokacin zaɓukan gwamna.

Jonathan ya yaba wa INEC, jami’an tsaro, jam’iyyun siyasa da al’ummar Jihar Osun bisa yadda aka gudanar da zaɓen gwamnan jihar cikin lumana.

Sai dai ya nuna damuwa kan yadda gwamnonin da ke kan mulki, manyan jami’an gwamnati da shugabannin jam’iyyu ke taruwa a jihohin da ake gudanar da zaɓe, tare da dimbin hadimai da jami’an tsaro daga wasu jihohi.

Ya ce irin wannan yanayi da aka gani a zaɓukan Osun, Ekiti da Ondo ba abu ne da ya kamata ya zama al’ada a tsarin dimokuraɗiyya ba, domin yana iya haifar da tsoro, razana da matsin lamba ga ’yan siyasa da masu zaɓe.

Tsohon shugaban ƙasar ya tuna cewa a lokacin da yake mulki, irin wannan lamari ya faru a zaɓukan Anambra na 2013 da Ekiti na 2014, inda ya ce ya bayar da umarnin manyan shugabannin siyasa da jami’an gwamnati su fice daga jihohin.

Jonathan ya gargadi cewa idan aka bar wannan salo ya zama ruwan dare, zai iya ƙara tsananta fafatawar siyasa tare da mayar da zaɓe tamkar fafatawar neman iko maimakon neman amincewar jama’a.

Ya jaddada cewa wannan ba batun Osun kaɗai ba ne, illa dai batu ne da ya shafi makomar dimokuraɗiyyar Najeriya baki ɗaya.

Saboda haka, ya yi kira ga National Peace Committee da ta shirya taron masu ruwa da tsaki da zai haɗa da INEC, jam’iyyun siyasa, hukumomin tsaro, Majalisar Ƙasa, NBA, Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya, ƙungiyoyin fararen hula da kafafen yaɗa labarai.

Ya ce irin wannan tattaunawa za ta taimaka wajen kafa iyakoki da ƙa’idojin gudanar da siyasa, kafin abubuwan da ake ganin ba su dace ba a yau su zama al’ada a gobe.

Dr. Goodluck Ebele Jonathan, GCFR, GCON
Tsohon Shugaban Tarayyar Najeriya (2010–2015)

Address

Sheme
Faskari

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A+A movement katsina chapter posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category