27/11/2025
Takaitaccen Tarihin Masanin Tafsirin Kur’ani, Marigayi Sheik Dahiru Bauchi
Daga Aliyu Usman Adam
Shahararren Malamin addinin Musulunci nan kuma daya daga cikin Khalifofin Shehu Ibrahim Inyass, wato Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasu safiyar yau Alhamis.
Sheikh Dahiru Usman Bauchi, malamin addinin Musulunci ne kuma jigo a Darikar Tijjaniyya na Afrika, bayan haka kuma mataimakin shugaban kwamitin koli na kungiyar malaman da ke bayar da fatwa a addinin Musulunci a Najeriya.
A shekarar 2019 wata hira da ya yi da dan jaridar jaridar The Punch, Armstrong Bakam, Sheikh Dahiru Bauchi ya bayyana wasu abubuwa dangane da rayuwarsa.
Da yake amsa tambaya a kan yadda ya zama babban malamin Tijjaniya, Sheikh Bauchi ya bayyana cewa, "ni bafulatani ne da aka haifa ranar 28 ga watan Yuni na shekarar 1927 a garin Nafada (da yanzu ke jihar Gombe), amma ni dan asalin garin Kwankiyel ne dake karamar hukumar Darazo a jihar Bauchi.
"Na yi dukkan karatuna na addini a karkashin kulawar mahaifina, har na haddace Qur'ani, kuma ta hannunsa ne na karbi darikar Tijjaniya. Shi mahaifina ya karbi darikar Tijjaniya ne ta hannun wani mutum mai suna Alhaji Gwani Abba.
"Daga baya sai mahaifina ya bani izinin na tafi duk inda nake so domin zurfafa ilimina na addini da haddar Qur'ani mai girma.
Shehin malamin ya zama masanin tafsirin Alkur'ani mai girma wanda ya samu lambobin yabo a wannan ɓangaren, ya kuma samu digirin girmamawa a bangarori daban-daban a najeriya sama faɗin duniya baƙi ɗaya. Ko a karshe shekaran data gabata wata gidauniya ta bashi lambar yabo da kuma babban jami'in tarayya dake garin lafia jihar Nassarawa sun bashi lambar yabo ta gigirin girmamawa.
Kadan daga cikin irin nasarorin da Shehu Dahiru Usman Bauchi ya samu a tsawon shekaru sa.
* Ya musuluntar da dubban mutane a wurin addinin musulunci a hannun sa.
* Shehi a duk lokaci bayan lokaci yana karanta Alkur'ani kuma sai yayi saukar Alkur'ani a kwana biyu.
* Shehi ya bada lazumin Darikar Tijjaniyya wa dubban mutane da dam