09/06/2026
Rashin Mutunci da Rashin Kunya na Wasu Matasa a Wannan Zamani 😭
Abin takaici ne yadda a wannan zamani wasu daga cikin matasa s**a mayar da shafukan sada zumunta wajen yaɗa bidiyoyi da hotunan da s**a saɓawa tarbiyya da ɗabi'un Musulunci.
Abin da a da ake ɓoyewa saboda kunya, yanzu wasu suna nunawa duniya gaba ɗaya ba tare da jin nauyin Allah ko na al'umma ba.
Allah Maɗaukakin Sarki yace:
﴿ إِنَّ الَّذِينَ يُحِبُّونَ أَنْ تَشِيعَ الْفَاحِشَةُ فِي الَّذِينَ آمَنُوا لَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ فِي الدُّنْيَا وَالْآخِرَةِ ﴾
"Lalle waɗanda suke son alfasha ta yaɗu a cikin muminai, suna da azaba mai raɗaɗi a duniya da lahira." (Suratun Nur: 19)
Haka kuma Annabi ﷺ yace:
"كُلُّ أُمَّتِي مُعَافًى إِلَّا الْمُجَاهِرِينَ"
"Dukkan al'ummata za'a yi musu afuwa sai waɗanda suke bayyana saɓo a fili." (Bukhari da Muslim)
Ya kamata matasa su sani cewa shahara ta hanyar yaɗa badala ba nasara ba ce, illa ce da za ta jawo fushin Allah, rushe mutunci, da lalata tarbiyyar al'umma.
Duk wanda ya taimaka wajen ɗauka, yaɗawa, ko kallon irin waɗannan abubuwa yana da nasa kaso na alhakin.
Iyaye, malamai da shugabanni suna da nauyin kula da matasa, basu tarbiyya, da kuma jan hankalinsu zuwa ga abin da zai amfane su a duniya da lahira.
Allah ya shiryar da matasanmu maza da mata, ya tsare su daga fitintinu na zahiri da na boye, yasa su zama abin alfahari ga addininsu da al'ummarsu.