30/04/2026
💥💥LABARI DA ƊUMI-ƊUMIN SA DAGA ABOKIN GWAGWARMAYAR JAM'IYYAR ADAWA 👇
🗣️Comrd Mudassir Adamu Daunaka 👇
SANARWA TA MUSAMMAN GA AL’UMMA DA MAGOYA BAYA
Ni, Mudassir Adamu, Coordinator Media na Gidan Dr. Bilyaminu Suleiman Ingawa Daunaka B/Kwari Ward, ina sanar da al’umma, abokai, magoya baya da duk masu bibiyar harkokin siyasarmu cewa:
Bayan sauyin sheƙar siyasa da Dr. Bilyaminu Suleiman Ingawa ya yi daga Jam’iyyar ADC zuwa Jam’iyyar APC, ina bayyana matsayina a fili cewa ban bi wannan sauyi ba, kuma ba zan sauya sheƙa tare da shi ba.
Wannan matsaya tawa ta samo asali ne daga cikakken tunani, fahimta da kuma biyayya ga akida da manufofin da na yi imani da su tun farko.
Shigata cikin Jam’iyyar ADC ba ta kasance don bin mutum ɗaya ba, illa domin kishin al’umma, gaskiya, adalci da kuma burin ganin an samar da siyasa mai tsafta da ci gaba.
A siyasata, na yi imani cewa akida da tsayawa kan abin da mutum ya gaskata su ne ginshiƙan mutunci da nagarta.
Saboda haka, ina tabbatar wa da dukkan magoya baya da abokan hulɗata cewa ina nan daram a cikin Jam’iyyar ADC, kuma zan ci gaba da bayar da gudunmawata wajen gina jam’iyyar da kuma tallafa wa manufofin da s**a dace da ci gaban al’umma.
Ina girmama kowane irin matsaya da kowa zai É—auka a siyasarsa, kuma ina yi wa kowa fatan alheri.
Allah ya ba mu ikon yin siyasa ta gaskiya, mutunci da kishin jama’a.
Na gode.
✍️
Mudassir Adamu