Arewa mufarka

Arewa mufarka Yan mufarka 🙏🙏🙏


Nigeria. ✊✊✊


Yanci zallah 👊👊👊

In Sha Allah. 🥰🥰🥰

18/06/2026

Tsaya Kaji 👂

JIYA BA YAU BA: Ali Kwara Jarumin Dazuka Na ArewaAli Kwara ba shi da uniform, amma sunansa ya kasance abin tsoro ga miya...
16/06/2026

JIYA BA YAU BA: Ali Kwara Jarumin Dazuka Na Arewa

Ali Kwara ba shi da uniform, amma sunansa ya kasance abin tsoro ga miyagu.

Ali Kwara, wanda aka fi sani da Alhaji Ali Muhammad Kwara, fitaccen ɗan Bauchi ne daga garin Azare a ƙaramar hukumar Katagum. Ya shahara a Arewacin Najeriya saboda jarumtar sa wajen yaƙi da ‘yan fashi, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka.

A rayuwarsa, Ali Kwara ya kasance ɗan farauta hunter mai haɗin gwiwa da jami’an tsaro k**ar ‘yan sanda da sojoji wajen bin sahun miyagun mutane a cikin dazuka. A lokuta da dama, ya jagoranci hare-hare tare da taimaka wa gwamnati wajen k**a manyan laifuffuka da kwato mak**ai daga hannun ‘yan ta’adda.

Ya yi fice musamman a jihohin Arewa k**ar Bauchi, Gombe, Katsina, Zamfara da wasu wurare, inda yake shiga dazuka yana bin sawun ‘yan bindiga domin ya tarwatsa su ko a k**a su. Wannan jarumta ta sa mutane da dama s**a fara kiransa da “Jarumin Dazuka” ko “Thief Catcher.

Ali kwara ya yi kusan shekaru 20+ yana aiki tare da hukumomin tsaro, yana taimakawa wajen gano miyagun mutane da kuma mika su ga ‘yan sanda domin shari’a. Duk da haka, bai kasance jami’in gwamnati kai tsaye ba, amma ya sadaukar da rayuwarsa wajen yaki da rashin tsaro.

Ali Kwara ba kawai jarumi ba ne a fagen yaki da laifi, har ila yau mutum ne mai taimako. A garin sa na Azare, yana ciyar da marasa galihu, yana tallafa wa marayu da zawarawa, har ma yana taimaka wa iyalai da mabukata ba tare da wata tambaya ba.

Tsawon shekaru da dama, ya shiga dazuka yana bin sawun miyagu, yana taimakawa jami'an tsaro wajen k**a masu laifi da kwato mak**ai.

Ba jarumi kawai ba ne, ya kasance mai taimakon marasa galihu, marayu da zawarawa a cikin al'ummarsa.

Wani abin ban sha’awa shi ne yadda aka rika cewa da zarar ‘yan ta’adda sun ji sunansa a yankin da suke, sai su tsere ko su wargaje, saboda tsoron sa da jarumtar sa.

A ƙarshe, ya hadu da iftila’in rashin lafiya har ya rasu a ranar 6 ga Nuwamba, 2020 a Abuja bayan fama da jinya.

15/06/2026

Saurara kaji👂

Au wai daman gwamnatin Nigeriya bata dau yan ta'adda a matsayin makinyanta ba duk da irin taddancin da suke? sun kashe m...
14/06/2026

Au wai daman gwamnatin Nigeriya bata dau yan ta'adda a matsayin makinyanta ba duk da irin taddancin da suke?
sun kashe mutanen da babu adadi
sun sace dabbobin da babu adadi
sun kwace dukiyar da babu adadi
sun sace mutanen da babu adadi
sun rautana mutane da babu adadi
Kuma duk basujiba basu gani ba.
duk da irin wadannan abubuwan da suke a kasa masu dauke su a matsayin makiyansu ba, sabo da ba ya'yan su da matansu da yan'uwa da dangin su ake sace waba. wannan ya isa ya nunar muku cewa mutanan bataku suke ba.

Zulum, Yana Daya Daga Cikin Gomnan a Arewa Tilo, da Ya saka aka K**a Yan Zanga zangan Tsadar Rayuwa . Ya Tilasata aka Ya...
14/06/2026

Zulum, Yana Daya Daga Cikin Gomnan a Arewa Tilo, da Ya saka aka K**a Yan Zanga zangan Tsadar Rayuwa . Ya Tilasata aka Yanke Musu Hukuncin Shekaru Biyar Biyar a Gidan Yari

Cewar Hamza nuhu dantani
Sannan ya kara da cewa
Laifinsu kawai shine , Sunyi zanga Zanga tsadar Rayuwa!!

Har yanzu Suna Rufe a Gidan Yari. Babu wanda ya tsaya musu ko yaje wajensu Don ya Tausaya musu. Iyalensu ne ke cikin wahalan gaske. Dayan kam Mahaifiyar ta Mutu saboda Bakin Ciki.

Duk da cewa Wasu daga Cikin Yan Zanga Zanga na wasu Jahohi, Gomnatin Tarayya ta bada Umurnin a Sake su…. wanda Yana daya daga cikin wanda Nayi fafutuka aka Sake su a Kano da Kaduna .

Hamza yayi tamabaya cewa
Tayaya, kake tunanin wani zai fito a Gari k**ar Borno yayi zanga zanga Akan Harkar tsaro ko kuma Yadda Yan Bindiga s**a sace yara a Makarantu a Askira Uba na jahar Borno ko kuma tsadara Rayuwa…..?

Ka saka mutum cikin Kuncin Rayuwa,!!!!, Ka Hana shi Tsaro, a Sace mishi Yan Uwanshi…. IDAN YA FITO ZANGA ZANGA , KA SAKA A KAMASHI , KA AIKASHI GIDAN YARI.

Nuhu dantani

Gaskiya Christopher Musa ya bani kunya wllh a lokacin da aka bashi ministan tsaron Najeriya nayi farin ciki sosai, mutan...
14/06/2026

Gaskiya Christopher Musa ya bani kunya wllh a lokacin da aka bashi ministan tsaron Najeriya nayi farin ciki sosai, mutane da yawa a Nigeria sun nuna farin cikinsu. Amma kuduba maganar da yake yi mara amfani. Yanzu gashi sun fara fakewa da yaƙin da ake da Iran akan matsalar tsaron kasarmu. To wllh duk sai kunyi bayani damin babu yadda za'ayi mubari kuci gaba da mulkarmu. Daga karshe ina mai yin Allah ya isa da farin cikin da nanuna lokacin da kazama ministan tsaro.

cewar angon mai awara

13/06/2026

Da mun san ciwon kan mu, mutuwar Gen. Rabe Abubakar a hannun ‘yan ta’addan daji ya fi k**ata.

Mutanen Arewa su fi maida hankali da tattaunawa a kai fiye da duk wani topic a halin yanzu.

Inji Bashir Ahmad

13/06/2026

Masu garkuwan sun mika gawar Janar Rabe Abubakar, sannan sun saki matarsa. Za a gudanar da sallar jana'izarsa a Katsina, k**ar yadda iyalansa s**a sanar.

Allah Ya jikansa da rahama. 🤲🏻

Address

K. Mazugal
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa mufarka posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share